MY BESTIE'S HUSBAND

*_Mbh_*


*_Ummuh Hairan_*


*_Wattpad-realfauzahtasiu_*


*_Telegram Link_*
            👇🏻
https://t.me/joinchat/Gdtmu0TgTHu66CF7


*_47-48_*


_____________________________
_____________________________


Shiru ce ta ratsa gurin na dan wani dogon lkc kowa zuciyarsa na searching abubuwa da dama mabambamta, zumbur Ja'afar ya miqe ya nufi qofa zai fita Mai martaba ya rufa masa baya shima Jamal miqewa yayi suka fita daga gdan duk wani guri da suke tunanin rafi'ah sun kasa samunta wasa wasa sai ga lkc yanata tafiya har goma na safiya shikam Ja'afar ya zamana kamar wani robbot ko bakinsa bai iya budewa sai tafasa da zuciyarsa takeyi.
Mai martaba ne yace da Jamal su juya suje gdansu Rafi'ah sugani ko taje can hakan ce ta faru suka nufi gidansu Rafi'ah Mai martaba yasa akayi masa sallama da Abba dake asabar ce Abba ya fito ganin Mai martaba da kansa yasashi qarasowa da saurinsa yanayi musu sannu da zuwa yanda yaga dum jikinsu  a sanyaye ya fadar masa da gaba yace “meye yake faruwa ne naga kamar Kuna cikin damuwa?"
Ja'afar ne ya magantu a karon farko yace “Rafi'ah batazo ba ko Abba shikenan na shiga ukuna ta shiga duniya Ina zataje hannun wa zata fada....." Jiri Abba yaji yana dibansa yayi saurin matsawa jikin motar yace “ban fahimta ba Ina Rafi'an ta tafi da danyan jego?"


Mai martaba ne ya zame rawaninsa ya goge gumi yace “wato yau mun tashi da wani iftila'i ne Alh Nuhu lfy Lau muka kwana da Yarinyar nan Amma da asuba sai ta tashi da wani yanayi me kama da samuwar tabuwar kwakwalwa hakan tasa mijinta yanke jiki ya fadi wai kafin a samu  a shawo kan tashi matsalar baa ankara ba ta sulale ta dauke danta ta fice munyi yawo sosai a garin nan tun asuba muke zagawa ko zamuyi katarin ganinta Amma Babu ita babu alamarta duk inda muka tambaya sai ace baa ganta ba to shine mukayi tunanin ko nan ta taho Kuma gashi alamu sun nuna batanan"
Durqushewa Abba yayi yana furta Hasbunallahu wani'imal wakil cikin mummunan tashin hankali miqewa yayi ya bazama gidan da sauri ya zaro wayarsa ya fito suka sake fita sune police station sune transport agent Amma Babu wani lbr me dadi saina godiyar Allah kawai ranar yini sukayi ko ruwa basusa a bakinsu ba Basu suka hqr ba sai taran dare suka koma gda kowa zuciyarsa cike da matsananciyar damuwa suna komawa gida Ja'afar ya shige bangarensa abin mamaki saiya tarar da Ni'imah a parlourn taci uwar kwalliya tana jiran dawowarsa.


Baikobi ta kanta ba ya shige ciki ya bude dakinsa tare da dauko key din daya dakin na Rafi'ah ya datse ya koma dakinsa ya haura kan gado ya hada tagumi yanajin wani zugi da radadin zuciya da bashi da misali baiji shigowarta ba saiji yayi tana wani shafa sumarsa ya dago idanunsa da suka kada sukayi jawur ya saukesu akanta take taji tsoro ya lullubeta Amma saita dake tace “we meye na tada hankalin hakane bafa wani hauka da takeyi tsabar iskanci ne dama ba sonka takeyi ba shine take neman hanyar rabuwa dakai cikin sauqi...."
Dagowa yayi ya sake saita injin idonsa akanta sosai take a tsorace Amma batason tabar zuciyarsa ta zauna kurum kamar yanda mahaifiyarta ta qyara Mata idan ya dawo tasan duk yanda tayi tasashi jin haushin Rafi'ah ta hanyar nuna masa tana sane ta Kama hauka don ta samu damar guduwar masa da dansa, hawaye ta dauke tace “na dade Ina jiye maka zuwan wannan ranar saidai Kai ka kasa fahimta Koda yake nasan bayin kanka bane asiri ne ke dawainiya dakai badon haka ba mema zakacj da Rafi'ah Ja'afar nidai Ina baka shawara ka cireta a ranka muci gaba da rayu....."


Tsawa ya daka Mata tare da daga hannu zai dauketa da Mari sai Kuma ya fasa ya miqe tare da shigewa bathroom ya sakarwa kansa ruwa yana furzar da iska ya fito tana zaune inda ya barta yaja dogon tsaki ya dauki doguwar rigarsa yasa ya fice daga dakin ya bude Wanda ya rufe dazun ya shiga ya tada sallar nafila ya nata jerawa ba qaqqautawa bayan ya idar ya jima yanayiwa Rafi'ah da Mahir fatan fadawa hannu na qwarai.
Alqur'ani ya dauka fara karantawa zuciyarsa na karyewa sosai yanajin yanda ruhinsa ke ciwo tabbas yasan a zaman da sukayi da Rafi'ah wata ukune kawai sukaji dadinsu watanni biyar duk sun tafi a banza ne to ko watsin da yayi da ita da rayuwarta a lkcn da tana da cikin ne yasats yanke Masa wannan hukuncin na rabashi da kanta da gudar tsokarsa Mahir?
Tambayoyine da bashi da amsarsu hakadai ya rinqa zauniya Koda yayi abinda ya sawwaqa cikin karatun qur'anin saiya rufe ya rafsa tagumi yanajin yanda jikinsa ke daukar zafi alamun damuwa ta fara ratsa bargonsa ta zuba Masa ciwon gabobi da zazzabi me zafin narkar da nutsuwar ruhi.Zamewa yayi ya haye gadon ya kwanta yanajin yanda jijiyoyin kansa suke wani tartsatsin wutar azaba qwanyarsa tana neman tarwatsewa gashi Babu mataimaki sai Allah yaji sanda Ni'imah ke buga qofar yayi Mata banza saboda baisan meye yasa ba tunda ya dawo Azare ya barota a Abuja ganinta ma bayason yi idanma ya kalleta gabansa faduwa yakeyi.


**********


Baiwar Allah Rafi'ah kuwa lkcn data fita daga gidan sarautar da asuba ta yanki shara a guje gudu takeyi na wucce saa da danta qunshe cikin towel ta sake qudunduneshi da hijjab dinta haka taketa keta dajin batare dako takalmi a qafarta ba haka take gudu a jeji gar ta fita daga Azare gabadaya ta shiga wani jeji me surquqi ta rinqa gudu ba qaqqautawa tana cilla qafarta ko Ina qaya zafin Rana baisa ta sunkuya, babban tashin hankalin idan ta waiwaya baya sai taga wuta naci a bayanta ganga ganga tana lasota haka zata qara zabura ta kwasa da gudu tana abbaton ya Khaliqu yini tayi ranar tana gudu babu ci babu sha ga cikinta inda akayi Mata aiki daketa azabar ciwo Amma Babu hankalin ta tsaya Abu daya da ya kasa mantuwa a ranta shine tasan idan taji danta ya motsa ta qara matsesa hankalin ta bashi abinci kuwa babu.
Ba ita ta samu ta daina ganin wutar ba saita ta wucce dambam ta shiga wani dajin shima shikuma ruwane yake binta da mugun gudu yanason cinyeta haka suka rinqa tsere da ruwan sai dare Allah ya kaita rugar wasu fulani da farko da suka ganta sun tsorata ita kuwa tana zuwa taga wata dattijuwa tana matsar nonon saniya sun hadawa shanu wutar jin dumi aikuwa sai ta nufi dattijuwar nan ta tsaya akanta matar ta miqe da sauri a tsorace ganin mutum a kanta murmushi tayi kamar me hankali sai ta yaye hijjab dinta ta budewa Mahir fuska ta miqawa dattijuwar ta bude baki zatayi mgn abin mamaki sai bakin ha harde ta kasa mgn.



Tayi tayi tayi mgn ta kasa kawai sai hawaye ya wanke mata fuska ta zube a gurin tanata kakari a dole mgn takeson yi ta kasa Abu daya da idan ta dage take iya fada shine Mahir Ya Khaliqu bayan wannan komai ta kasa furtawa, nan fah gurin ya cika taf da mutanen rugar daidai lkcn da wata arniyar mota ta parkar a bayansu kadan an jima baa fito ba can aka bude aka fito wani kyakkyawan matashin attajiri ne a qallah zaiyi shekaru arba'in da biyar ya nufo rugar dauke da wata jarka a Hannunsa mamaki ya cikashi na ganin yanda mutanen rugar suka kewaye guri guda,
Hakan yasashi saurin qarasawa idonsa ya sauka akan Rafi'ah da ta hada uban tagumi tanata gunjin kuka so takeyi tayi mgn ta kasa hakan yasata dole ta Kama kuka tsayawa yayi daga baya kadan ya zuba Mata idanunsa a mamakance ya juya ya kalli wani mutum yace “Moddibo wannan fah daga Ina?" Dagowa Moddibo yayi yace “wlh bamu sani ba kawai yanzun nan tazo ta miqawa Gwaggo Hinde jaririn can tanata qoqarin mgn Kuma ta kasa" sake kafeta yayi da ido ya matsa gabanta ya tsugunna yasa hannu ya dago kanta Saida gabansa ya fadi ganin irin kyawunta da quruciyarta kawai sai ta fada jikinsa ta sake sakin  wani kuka tana shan zuciya tuni zuciyarsa ta karya ya cika da tausayin baiwar Allan tabbas yanayinta ya nuna ba daga qaramin ahli ta fito ba, haskata yayi sosai da fitilar wayarsa tana kwance a jikinsa ya dago ya kalli Gwaggo Hinde yace “Ina tunanin Jaririn nan dantane kijata ki kaita dakinki ki bata abinci da ruwa tayi wanka amma ta fara shayar da jaririn Nan akwai wani boyayyen qulli cikin lamarin yarinyar nan idan ta huta zuwa safiya zanzo zan dauketa na tafi da ita Gombe"


Tsalle Hinde tayi taja baya tace “Oye aradun Allah banni samkarta Niko shedai ka tahi da itan tun yau hakanan abuda munaji a gari ana yanke kawunan mutane nasani ko aikota akayi ta yanke kaina don anga zayayi tsada....” saurin kallonta yayi yace “haba Gwaggo da ganin yarinyar nan kinsan badaga qaramin gida takeba Kuma tana buqatar taimako idan kika taimaka Mata kema Allah zai taimakeki Kuma bakisan abinda Allah ke nufi ba ya kawota nan rugage nawa ta tsallake bata tsaya ba sai anan"
Sake ja tayi da baya tare da miqa masa jaririn tace “kaidai da kaji kana iyawa ka dauka nikam bani iyawa...." Alh Hashim irin mutanen nan ne masu zuciya kawai saiya Kama hannun Rafi'ah ya miqar da ita yace “ok ki zubamin danyar madara a kawomin mota Amma ki taimaki yaron nan ki bashi ko danyan nono ne dafaffe yasha akwai alamun bata Sami hayyacin bashi abincinsa ba" shima Hinde taso ta musa Saida Moddibo ya shiga mgnr sannan ta yarda ta dauko qaramin Kofi ta tsiyayo dafaffiyar madarar shanu Moddibo ya kawo Zuma akasa a ciki akayi kwakkwaro da ganyan ayaba aka zuba aka rinqa bawa yaron Allah Sarki bawan Allah har wata ajiyar zuciya yakeja yanasha yana lumshe ido.


Tausayi ya cika Alh Hashim yanda yaga Rafi'ah ta zubawa jaririn ido duk da kukan da takeyi Saida alamun murmushi suka bayyana a fuskarta tausayinta ita da yaron yasa baisan sanda hawaye ya rinqa zarya a idonsa ba yaron Yana gama sha taja wata ajiyar zuciya ta janye daga riqon da yayi Mata ta matsa ta karbi danta ta rungume a gurin babu wanda Bai zubar Mata da hawaye ba soyayyar da da mahaifi wato ko mahaukaci yasan jininsa kama hannunta Alh Hashim yayi yakaita motarsa ya bude yasata a ciki.
Shiga yayi yaja suka tafi tunda suka taho ta sunkuyar da kanta take ajiyar zuciya shima baice mata komai ba yaci gaba da tuqinsa yana saqa abubuwa da yawa yanzu ahalinta sunanan sunata nemanta ruwa a jallo shikuma gashi Allah ya bashi numfashi ya sauke sukaci gaba da sharara tafiya itai bacci ne ya dauketa batasan sanda suka isoba saida taji ana bugun kujerar da take Kai tayi firgigit ta farka wani abin mamaki sai ta bude baki da ambaton "A'uzubillahi minasshaidanur rajim" mamaki ne ya cika Alh Hashim ya dubeta da sauri yace “ya sunanki?" Zuba masa ido tayi tare da kallon yaron tace “Mahir" sai Kuma ta fashe da kuka jikinsa yayi sanyi ya miqa hannu ya karbi yaron ya bude Mata qofa ta fito saime?
Basai qafa taqi takuwa ba tayi saurin riqe cikinta ta durqushe tace “way.... Wayyohhhh cikina zaz....zai bude ahhhhhhh....." Da sauri Alh Hashim ya iso gareta ya riqota ya sake sakata a mota suka Kuma ficewa daga gdan sai Gombe General Hospital shigar da ita akayi don har ta fice daga hayyacinta suka fara checking dinta da farko sun bata lkc Basu gano matsalarta ba sai suka bige a ciccire Mata qayoyi da kwalaben da ta tattaka a qafarta Saida suka gama wata cikin nurse din ta lura da rigarta data jiqe da wani ruwa me hade da jini jini ta daga rigar da sauri saiga bandege ya jike sharkaf da ruwan miki"


Nan fa suka fita suka sanar da Alh Hisham halin da ake ciki suka shigo tare suke fada masa sai an sake Mata gyaran aikin sabida alamu sun nuna ya balle Allah ne ma yayi da kwananta a gaba da tuni ta daina shaqar iskar duniya, nan take yasa hannu aka shiga da ita dakin Teather a lkcn dare yayi nisa waima don da sanayya ne dake ba boyayyen mutum bane shi a fadin Gombe a mota ya kwana da Mahir idan yaron ya farka sai ya lakata masa Zuma a bakinsa haka suka kwana shidai baiyi bacci ba ya lalace a kallon mahir yanajin dama ace dansane na cikinsa shi ko shegene goye abinsa zaiyi gefe daya Kuma yana tunanin yanda akayi mijin wannan baiwar Allah ya bari ta subuto daga hannunsa da danyen jegonnan tabbas ba banza ba bayan tiya akwai wata caca.
Tunanin abubuwa da yawa ya hanashi gane gari ya waye Saida aka qwanqwasa glass din motar ya dawo hayyacinsa ya dago ya bude Dr Zubair ne yace “ranka ya dade wannan baiwar Allah da alamun ta dan taba gushewar hankali alhmdllh ta dawo hayyacinta saidai fah kamar tayi loosing memory's dinta na baya Abu biyu naji tana furtawa Mahir Ja'afar and tana buqatar kulawa sosai don Allah kada a qara bare ta fita qafafunta akwai ciwo don ba daidai ta koma ba Amma na'urorinmu sunkasa gano Inda ta samu matsala a brain dinta saidai abin bashida qarfi sosai idan ta samu kulawa ma zai gushe da Kuma addu'a"


_More comments_
_More Typing_


*_Ummuh Hairan_*

Comment