MY BESTIE'S HUSBAND

*_My Bestie's Husband_*




*_Ummuh Hairan_*




*_Wattpad-realfauzahtasiu_*



*_27-28_*



_____________________________
_____________________________



Daqyar da dabara saboda bayason wahalar da ita ya samu ya cimma burinsa ya saki wata ajiyar zuciya tare da dakatawa duk da dama bai yarda da mgnr su Barebari ba Amma zuciyarsa ta danyi dar saboda yasan abokin damo guza tabbas idan ta kasance aminiyar Ni'imah to komai zata iya faruwa amma sai gashi ya sameta asalin Varging duk da itama Ni'imah ya sameta da budurcinta Amma baikai qualityn na Rafi'ah ba duk masifarsa bai iya shigarta gabadaya a wannan dare ba kamar yanda ya shigi Ni'imah a daren farko.
Wani tausayinta ne ya kamashi jin yanda take kuka tana jujjuya kai tana Kiran iyayenta, ji yayi bazai iya cigababa sarai ya fahimci ba qaramar wahala zasusha ba daga ita harshi gata itanma Masha Allah akwai dauriya amma wannan abun yafi gaban dauriya saidai dabara, janye jikinsa ya farayi a hankali ya koma ya kwanta a gefenta yanajin sinadirun qaunarta yana qara zagaye duk wani bangare na jikinsa a hankali ya janyota jikinsa lkcn da wasu hawaye suka zubo masa ya rungumeta tare da hura Mata iskar bakinsa a kunnenta da haka bacci yayi ram da ita.



Ya dade yana kallonta ita komanta me kyaune yana godewa Allah da yayisa cikin mutane masu saa yasan aurenshi da ita ba qarfinsa ko isarsa bace kawai lucky ne da yake dashi a rayuwarsa da wannan bacci ya daukeshi shima, Kiran farko ta farka tajita tsam a jikinsa ta rinqa motsawa har ya tashi bai bude idonsa ba sai sakarta da yayi ta zura qafafunta qasa ta taka saiji tayi wani zugi ya ratsa qasanta ta cije ta miqa hannu ta dauko kayanta ta daura zanin a qirjinta ta rinqabin bango ta samu ta shiga bathroom din tayi wanka ta tsaftace jikinta tanajin zafi idan takai hannunta gurin hakadai ta gama ta dauro alwala ta fito.
Wardrobe ta bude wani sanyin dadi ya shigeta ganin kayanta a jere a ciki ta zaro doguwar riga da hijjab tasa ta shimfida sallaya ta tayar da sallah raka'atainul fajri tayi ta zauna tana istigfari ta yarda cewa istigfari shine mabudin dukkan wani alkhairi na duniya saboda shine abunda yake goge maka duk wani zunubinka ya kusantaka da Allah salin alin.



Ta Jima tana roqon Allah sanyi zuciya da ikon yiwa mijinta biyayya kamar yanda kowa yake horonta domin ta haqiqance aikin gama ya riga ya gama bata fatan shiga haqqinsa ko zata cutu tanason tayi Masa biyayya kamar yanda Allah ya hukunta bai isheta hujja ba a ranar qiyama tace da Allah saboda batasonsa ko don ya kasance mijin aminiyarta ne yasa taqi bin dokokin sa taqi yin biyayyar aure ba.
Miqewa yayi cike da nishadi ya samu kalar matar da yake mafarkin mallaka shekara da shekaru batada ganda wajen bautar Ubangiji tabbas Allah yanasonta shiyasa ya sanya duk wani mumini yake sonta, shima tsaftace jikinsa yayi yazo yayi salatul Fajri sannan yajasu sukayi asuba bayan sun idar kowannensu yayi azkar ya miqa Mata hannu noqewa tayi yayi murmushi yace “mafi alkhairin gaisuwa itace musabaha tare da sallama My Bestie ki saba ni gaisuwata kenan"
Yana fadin haka ya miqe ya cire doguwar rigarsa ya rage dagashi sai boxes ya matso ya dagota ya cire Mata hijjab din ya fara qoqarin cire Mata rigar ta riqe hannunsa tare da dago manyan fararen idanunta ta zubasu a kansa cikin saar lillahi suka fada cikin nasa yaji wani tartsatsin wutar qauna da feels gami da kwarjini sun kashe Masa jiki yayi kamar ya saketa ya fasa yace “akwai zafi kada ki takurawa kanki ki jure zaki dace inason kasancewa da iyalina a kowacce asuba hakan yanasa na yini cikin farin ciki don Allah kada ki batamin yinina a hankali zanbiki kedin special ce Rafi'ah"



Sosai gabanta ya tsananta faduwa tsoro ya dirar Mata tana tuno irin wahalar data dandana daren jiya idan yace zai qara yimata haka tana tunanin mutuwa zatayi.... Bai bata damar gama tunanin ba ya dauketa ya azata a gadon ya kashe musu glove din yayi musu cover da  duvet babu abinda ke tashi a dakin sai shassheqar kukanta da nishinsa yanata zuba Mata sannu duk wata gaba ta jikinta Babu inda bai galabaita ba kafin ta samu yayi release ya kwanta luf a jikinta itakam tuni takai China a sume ya rinqa kwarara Mata ruwan albarka yana yabawa da baiwar da ilahi yayi Mata Saida ya saitu sannan ya fahimci halin da take ciki ya zare jikinsa a hankali daga nata ya dauko ruwa me sanyi ya rinqa shafa Mata.
Yanajin tayi ajiyar zuciya shima yayi bata bude idonta ba sai kukanta da taci gaba dayi ya shafa fuskarta yace “Sorry please zaki saba kinji matata Allah yayi miki dawwamammiyar albarka kin jiyar dani dadi yau ke ta dabance komanki dabanne" tashi yayi ya nufi bathroom ya hadanta ruwa yazo zai dauketa taqi dole yana kallonta ta zura hijjab dinta ta nufi bandakin tana dafa bango tana cije lebe yana kallonta cike da tausayi tana zuwa ta gasa jikinta tana kuka saboda azaba tayi wanka ta fito ta zauna saman drees stool ta dauki doguwar rigarta ta haye gadon daya cire bad sheet din ya shimfida wani ta kwanta tana jin dacin abubuwa da yawa a ranta da haka bacci ya dauketa batasan sanda ya dawo ba shima yayi wanka ya kwanta ya janyota baccin ya daukesu tare basu suka farka ba sai 11 saboda sunji jiki daga ita harshi inda uwargida Ni'imah takecan ta hadiyi baqin ciki da tashin hankali da asubar Mom ta kirata cikin dimuwa tace.



“Ya akayi baki binne layar da boka Na gangare ya bayar aka kawo miki ba yanzu gashinan kin rusa Mana aikinmu komai da baaso ya faru ya faru tsakaninsu" cikin gigita tace “bam.... Bangane ba naga a gabanki na binneta" dafe kai Mom tayi tace “to ya haka yanzu boka ya kirani yake fadamin yanzu aljanin daya tura ya dawo masa a galabaice ya kasa isa ga Ja'afar din duk sanda yayi yunqurin tabashi sai yaji kamar ana yayyafa masa ruwan tafasau ita Kuma Rafi'ah itama lkcn da ta tashi da asuba tayi sallah tayi addu'a shiyasa ya kasa kaiwa gareta Kinga zamufi samun sauqin tabata akanshi shidai kinsani batun yau muke barnar kudi akansa mun kasa samun galaba ba kawai aikinmu ya karkata kanta ita daya shi mu qyaleshi boka na gangare yace tabbas idan muka cika matsawa akan Ja'afar to kwabarmu zatayi ruwa domin kuwa yanada dafa'i irin nasu na gdan sarauta da baya bari su tabu"



Tuni Ni'imah ta fita daga nutsuwarta ta Kama kuka kamar wata zautacciya tana cewa “ai Kuna sane kuka bari komai ya faru tunda kunada ikon hanawa kun hanani daukar mataki a hannuna sannan Kuma kunqi dauka wlh bazan iya zama inuwa daya da Rafi'ah ba duk muna amsa sunan Matan mutum daya ba dole sai ta fita tabarmin gidana...." Katseta Mom tayi da cewa “abinda boka ya kasayi shine ke zakice zakiyi ta yaya? To bari kiji kada ma ki fara kinji dai da kunnenki abinda bokayennan uku sukace idan kika matsa kece zaki tafi kibar mata gidan ke Kuma shegiyace ke da zaki bari kishi yasa kiyi asarar zamanki matar sarki me jiran gado to tun wuri ma ki nutsu da ace zaki iyama da kin daina wannan haukan kinbi komai a sannu kin shiga jikinsu ta yanda zakifi yimusu illah"
Cikin shassheqa tace “bazan iyaba Mom ni bazan iyaba kawai ayi duk wacce zaayi na tsani Rafi'ah wlh ganinta ma zai iya sawa na kashe kaina yanzu fah banida wata taqama da zanyi Mata tasanni tasan sirrina dama da mijin zanyi Mata balli to shima tasanshi tasan komai dana sani game dashi nikam Mom bazan iya hqr da wannan baqin cikin ba...."  Takaicine yasa Hajiya Sahura kashe wayarta ta rasa wacce irin ya Allah yabata da batajin shawara ana nuna Mata annabi tana rintse ido koda suke taqama da asiri wani abin sai an hada da kirsa gashi Ni'iman taqi ganewa sai shirme takeyi




Tananan zaune tanata aikin kuka ya shigo da sallamarsa mamaki ne ya kamashi ganin da gaske kuka takeyi ya zauna kusa da ita ya dora hannunsa a bayanta yace “barka da safiya uwar gida" dagowa tayi idanunta na zubar da hawaye tace “da gaske ka kwanta da Rafi'ah Ja'afar don Allah gaske ne?" Sakin baki yayi da tsananin mamakin yanda akayi ta sani, Kama hannunsa tayi tace “ka fadamin Ja'afar ka kwanta da ita kayi Mata duk abinda kakeyi min?"
Murmushi yayi ya kamo fuskarta yace “Eh hakane harma fiye da abinda nakeyi Miki nayi Mata meye damuwarki matatace inada ikon nayi komai da ita kamar yanda zanyi da ke koma fiye da haka"
Miqewa yayi ya zaro kudi ya bata yace “zanje asibiti na dawo bamata da lfy don daqyar ma nasamu taci abinci" harara tabisa dashi har ya fice taja dogon tsaki tace “shashasha Allah ya kasheta ma kowa ya huta" yana fita ta dauki mayafinta itama ta sauko qasa dakin da samiha ta kwana tace “fito mu tafi zanje na samu Uwarsa na fada Mata gara taji ta sani bazan dauki wannan wulaqancin ba harni Wai zai duba ya fadawa wai yar iskar matarsa batada lfy?"



Murmushi Samiha tayi tace “kinada matsala To yanzu idan kinkai Mata qararsa me zatayi Masa?" Tsawa ta daka Mata tace “idan zaki kizo mutafi kawai" miqewa tayi suka fita a mota lkcn Rafi'ah tadan tashi tana leqowa qasan ta window tana kallonsu suka shiga mota suka fita ta lallaba ta sauko qasa ta dan gyarashi ta shiga kitchen gashinan komai kamar banza an zuba matashi badon tanajin dadin jikinta ba saidon sabo ta fara girkinta tanajin nishadi duk gdan ya cika da qamshi, ji tayi an riqeta ta baya ana sunsunar wuyanta tadan tsorata amma jin qamshinsa yasata sauke ajiyar zuciya ya juyota suka kalli juna yayi Mata murmushi tare da kissing  goshinta yace “me kike girka mana?" Sunkuyar da kanta tayi tace “barka da dawowa" wani farin ciki ne ya cikashi ya sake matseta yana shafa bayanta yace “yawwa my bried ya gda" bata bashi amsa ba sai qoqarin janyewa da takeyi yayi ajiyar zuciya yace “kamata yayi ace nazo na tarar dake a kwance kina hutawa ba a kitchen ba" sake sunne kanta tayi a qirjinsa yaja numfashi yace “hakanma yayi matata bari na tayaki tunda na dawo amma dai baki manta ba yau akwai dinner da dare..."


Girgiza masa Kai tayi tace “aa" Dagota yayi yace “aa me?" Qasa ta qarayi da kanta tace “bazan iya zuwa ba" zamewa tayi daga jikinsa ta nufi inda take gyaran nama yabi tafiyarta da kallo yayi murmushi yace “saboda kada a gane alif ya dauri fataha shine zaki batamin burget dina nagadai a hankali ma nabaki kika karba" kunyace ta lullubeta taqi ce masa komai tanajin kamar ta nutse cikin qasa yayi murmushi yace.
“Kada ki damu dama yanzu daga gurin Abba nake nace masa bakida lfy so babu me zuwa daga bangarena har bangarenki hutawa zamuyi sosai mu gama girkin mu fita mu zaga gari ko?" Harararsa tayi yayi dariya me sauti yace “inason harararnan masifar kyau takeyi miki" ganin da gaske ya zage yana tayata aikin yasata dagowa tace “ni don Allah katafi ka kwanta kabarni nayi aikina" dago idanunsa yayi yayi Mata kallon daya sata saurin shiga taitayinta, kafin tayi mgn sukaji an turo qofar parlourn an shigo ta kalleshi shima ya kalleta gabansa yabada wani rass jin sautin Mahaifiyarsa tanata kutuntume kutuntumen ashar wani abu yaji ya caki maqoshinsa yayi saurin riqota tana Shirin fita sama Hajiyan tahau shikuma yayi saurin rufe qofar kitchen din yasa Mata key ya dora Mata hannu a baki yace “rabudasu kada kice komai muci gaba da aikinmu" itadai duk jikinta rawa yakeyi ya lura da tsoronta shiyasa ya sake shigar da ita jikinsa ya murde gas din ya dora harshensa saman fatar kunnenta yana lasa a hankali ji sukayi Sun sauko Hajiyan tana cewa “qyaleni da sallamamme ya dauketa sun fice daga gdan yo budurwar arziqi ce zatasan namiji jiya har tasamu qafar yawo wlh saiya Raina kansa sakarai kawai" hawaye ne ya zubo a idanun Rafi'ah shikam Ja'afar bai daina abinma da yakeyi ba yayi biris kamar bayajinsu yana murza qirjinta dakeyi Mata wani azabar zafi a hannunsa yana tsotsar kunnenta da salon rikita lafiyyar mace janyewa yayi jin parlon yayi tsit alamun sun fita ya bude qofar yaje ya dannawa ta parlourn key ya dawo sukaci gaba girkinsu tun tanajin ciwon tijarar da Hajiya Fatsum tazo yimata har tama manta yana manne da ita suka gama girkin ta sulale ta haye saman tayi wanka ta shirya cikin atamfa doguwar riga tayi kwalliyarta simple ta sake saukowa ta zauna a parlourn tana kallo shima saukowa yayi ya iso gabanta ya dagota suka nufi dinning din shi ya rinqa ciyar da ita bayan sun gama ya miqe ya haura saman ya sauko Mata mayafinta da wayarta ya miqa Mata ta yafa ya kamota suka fice ya bude Mata motar ta shiga daidai lkcn Hajiya suka fito ita da Hajiya Sahura suka tsaya sakatoto suna kallon ikon Allah Saida ta shiga ya kulle sannan ya qarasa ga su Hajiyan ya rusuna suka gaisa tace “dama Kuna ciki mukazo kukaqi budewa?" Shafa kansa yayi yace “eh wlh muna dakin qasa dake batada lfy so Ina qoqarin sanyata tai baccine lkcn shiyasa yanzun ma zamu zaga garine" bai jira cewarta ba ya miqe yace “to Hajiya agaida gda mun gode da ziyara zan kawo miki ita har gida yanzun tana buqatar hutune hayaniya damunta zatayi"..........




_More comments_
_More typing_





*_Ummuh Hairan_*

Comment